Skip to main content

Sakon Jaje Zuwa Ga Mutanen Zamfara Daga Bakin Sen. Saidu Muhammad Dansadau

Sen. Saidu Muhammad Dansadau yana zubarda hawayensa akan abunda yake faruwa a Jihar Zamfara. Sannan Kuma ya umarce ni da na isar da sakon jajantawa akan Iftila’in da ya faru ga Al’ummar: JANGERU KWARE KURYA KURSASA BADARAWA ZANGEME  GURBIN BORE KAURA  SHINKAFI  ZURMI TSAFE MARADUN Da Zamfara Baki Daya da sauran Kauyukan Zamfara wadanda Masifa da zubar da Jini Tare da Garkuwa da Mutane wadanda ta shafa. Wannan Masifa abar dubawa ce ya kamata Gwamnatin Jaha da Mahukunta su tashi tsaye domin ganin cewa an kawo karshen wannan masifa.  Sen. Saidu Muhammad Dansadau yasha alwashin Idan Allah yasa yayi Nasara matsalar Tsaro ita ce Abu na Farko da zai Magance da Izinin Allah. Muna Fatan Allah yaba Sen. Saidu Muhammad Dansadau a Matsayin Gwamnan Jihar Zamfara 2019. Allah ya bamu zaman lafiya a Jihar mu da Kasa baki daya.   
Programmers Association of Zamfara state πŸ‘¨‍πŸ’»πŸ‘©‍πŸ’»

Comments

Popular posts from this blog

FAHIMTAR DA MUKAYI WA HALAYE DA KUDURORIN SEN. SAIDU MUHAMMAD DANSADAU

FAHIMTAR DA MUKA YIWA HALAYE DA KUDURORIN SEN. SAIDU MUHAMMAD DANSADAU Bayan kammala nazari da bincike tare da tuntuba  da neman shawarwari cewa a halin da siyasar jihar Zamfara take ciki a yau, babu wani mutum wanda ya cancanta da jagorancin jihar a 2019 don ceto al’ummar Zamfara sai Sen. Saidu Muhammad Dansadau, Gamji sha sassaka, gagara tarkon mahassada, sawun giwa badda na rakumi, bauna mai tafiyar kasaita, gugar karfe garnakaki, hadarin sama sai saurare, madugun nasara, sadauki, adili, mai gaskiya da rikon amana, haziki, jarumi, mai juriya, mai hikima, mai hakuri,  mai son zaman lafiya, mai farin jini abokin kowa, gogaggen dan siyasa kuma masanin siyasar zamani, mai tausayin talakawa da kishin al’ummar jihar Zamfara, masanin makamar aiki, mai kyakkyawar manufa kuma dattijo a furucinsa da ayyukansa tare da dalilan da yasa muka zabe shi a matsayin wanda ya kamata mu mara wa baya domin cimma kuduroran da muka sanya wa gaba. Sako Daga........ Programmers Association...

DANSADAU STUDENTS ENLIGHTMENT FORUM

    Amadadin Wannan Kungiya Mai Suna Asama Tare da Dantakarar Governor Zamfara State karkashin jam’iyya NRM National Rescue Movement  Waton Sen. Saidu Muhammad Dansadau     Suna  Farin Chikin gayyatar Al’ummar Jihar zamfara Zuwa Wajen Taro Wadda za’ayi kamar haka Rana:5th February 2019  Dakin Taro : maryam multipurpose  Hall Gusau / Tudun wada zamfara State Time: 9:00 πŸ•˜   For more Information contact Us  08034213555/07068519179  Programmer Association of zamfara state πŸ‘©‍πŸ’»πŸ‘¨‍πŸ’»*

Zan Kula Da Harkar Lafiya Idan Allah ya Yarda.......

Assalamu alaikum Al’ummar jahar Zamfara masu girma da daraja, Ni Sen. Saidu Muhammad Dansadau ina mai sanar daku cewe Idan Allah ya bamu nasara a Zaben 2019 zanyi iya kokari na bada kulawa sosai a kan harkar Lafiya duba ga rashin kulawar Gwamnati a harkar, Idan Allah ya yarda zamuyi Iya Kokarinmu na mun samar da Asibitoci a cikin Birni Da Karkara dake fadin Jihar Zamfara, Bayan haka zamu bada Magunguna Kyauta Ga marasa lafiya da wadanda basu da karfi Da Izinin Ubangiji. Ku zabi Sen. Saidu Muhammad Dansadau domin ceton Jihar Zamfara. Sako Daga: Programmers Association of Zamfara StateπŸ‘©‍πŸ’»πŸ‘¨‍πŸ’»