Skip to main content

RUWA RUWA RUWA BABA!!!




 ZANKULA DA HARKAR RUWA IDAN HAR ALLAH YA BANI GOVERNOR 2019 INSHA ALLAH INJI SEN. SAIDU MUHAMMAD DANSADAU.
                 
 Bani Da Burin Da Yafi Naga Na Samar Da Ruwan Sha Ingantattu A Zamfara, Domin Inajin Bakin Cikin Safiya Ta Waye Amaimakon Kaga Yaro Yanufi Hanyar Zuwa Makaranta Sai Yanufi Hanyar Nemawa Uwayensa Ruwan Sha   Gaskiya Wannan Abun Yana Ban Haushi Wanda Koda Yaushe Banida Buri Irin Naga Na Inganta Rayuwar Jihata Ta Zamfara. A Koda Yaushe Ruwa Sun Kasance Tamkar Sune Rayuwa Ta Dan Adam Idan ba Ruwa ba Rayuwa, Da Wannan Dalilin ne Yasa Nakeso Na Kula Da Ruwa Insha Allah Domin Matsalar Ruwa Ta Zama Tamkar Matsala Abar ‘Kawa Koda Yaushe Bani Burin Gina Gida Ko Na Hau Mota Illah Naga Na Inganta Yankina Da Ababen More Rayuwa Kamar Yanda Sauran Makwotanmu Suke Irinsu Sokoto, Kebbi Kaduna, Katsina Da Dai Sauran su. Wannan Shine Burina Insha Allah Ina Rokon Allah Ya Cika Muna Wanann Buri Namu Na Alheri.
Ameen.

Gwamnan Gobe Da Yardar Allah Taken Babanmu Shine: *RUWA RUWA BABA* ZAMU SHA RUWA DA KYAU INSHA ALLAH.

 _PROGRAMMERS ASSOCIATION OF ZAMFARA STATE 👩‍💻👨‍💻_

Comments

Popular posts from this blog

Da Mune Mukayi Shekara Takwas (8) Muna Mulki A Zamfara, Da Mafi Yawan Mutane Sun Samu Aikin Yi

'Dan takarar Gwamna a jam'iyyar NRM a jihar Zamfara, Sanata Sa'idu Dansadau ya bayyana cewa matukar suka shekara takwas kan mulki, to duk Dan jihar zamfara sai ya sami aikinyi. 'DanSadau ya bayyana hakan ne a lokacin da yake kaddamar da gangamin yakin Neman zabensa, da ya gabatar a garin Gusau ta jihar Zamfara. Ya kara da cewa idan ka dubi Zamfara shekara Ashirin da suka wuce, sai ka zubda hawaye, saboda yadda zaka ga matasa suna yawo babu aikin yi, kuma ya ce mafiya yawansu duk sun yi karatun boko. Dan takaran na Gwamna ya kara da cewa matukar al'ummar jihar zamfara suka zabi wannan Jam'iyya  ta NRM, to kowane Dan zamfara sai ya sami aikinyi , kuma sai an dinga zuwa Kaduna ko Kano ana dauko ma'aikata saboda a basu aikinyi. Da ya koma kan matsalar tsaro ya ce ya zama wajibi ga al'ummar jihar zamfara dasu fitone kwansu da kwarkwatansu don yakar Azzalumai, sabo  da Allah baya son zalunci. Ya ce kama daga Azzalumai masu kwashe kudin al'umma...

Zan Kula Da Harkar Lafiya Idan Allah ya Yarda.......

Assalamu alaikum Al’ummar jahar Zamfara masu girma da daraja, Ni Sen. Saidu Muhammad Dansadau ina mai sanar daku cewe Idan Allah ya bamu nasara a Zaben 2019 zanyi iya kokari na bada kulawa sosai a kan harkar Lafiya duba ga rashin kulawar Gwamnati a harkar, Idan Allah ya yarda zamuyi Iya Kokarinmu na mun samar da Asibitoci a cikin Birni Da Karkara dake fadin Jihar Zamfara, Bayan haka zamu bada Magunguna Kyauta Ga marasa lafiya da wadanda basu da karfi Da Izinin Ubangiji. Ku zabi Sen. Saidu Muhammad Dansadau domin ceton Jihar Zamfara. Sako Daga: Programmers Association of Zamfara State👩‍💻👨‍💻

Sakon Jaje Zuwa Ga Mutanen Zamfara Daga Bakin Sen. Saidu Muhammad Dansadau

Sen. Saidu Muhammad Dansadau yana zubarda hawayensa akan abunda yake faruwa a Jihar Zamfara. Sannan Kuma ya umarce ni da na isar da sakon jajantawa akan Iftila’in da ya faru ga Al’ummar: JANGERU KWARE KURYA KURSASA BADARAWA ZANGEME  GURBIN BORE KAURA  SHINKAFI  ZURMI TSAFE MARADUN Da Zamfara Baki Daya da sauran Kauyukan Zamfara wadanda Masifa da zubar da Jini Tare da Garkuwa da Mutane wadanda ta shafa. Wannan Masifa abar dubawa ce ya kamata Gwamnatin Jaha da Mahukunta su tashi tsaye domin ganin cewa an kawo karshen wannan masifa.  Sen. Saidu Muhammad Dansadau yasha alwashin Idan Allah yasa yayi Nasara matsalar Tsaro ita ce Abu na Farko da zai Magance da Izinin Allah. Muna Fatan Allah yaba Sen. Saidu Muhammad Dansadau a Matsayin Gwamnan Jihar Zamfara 2019. Allah ya bamu zaman lafiya a Jihar mu da Kasa baki daya.    Programmers Association of Zamfara state 👨‍💻👩‍💻